Innalillahi Wa’inna Illaihir Raji’un! Labarin Amaryar Data Rasa Idonta Guda Daya Ranar Daurin Aurenta, Wata Amarya Mai Suna Khadija Abdullahi Ta Kakance A Ido Ɗaya Sakamakon Zabga Mata Gora Da ‘Yan Ƙato Da Gira Su Yi A Ranar Daurin Aurenta.
Wannan Iftila’i Ya Faru Da Amarya Khadijah Ne Lokacin Ana Tsaka Da Shaglin Bikin Aurenta A unguwar Ɗantamashe Da Ke Birnin Kanon Dabo.
A Cewar Khadija Ƴan Kungiyar Sintiri Na Vigilante na Unguwar Tasu Sun Mata Wannan Aika-Aikan Lokacin Da Suje Raraka An Tsaka Da Kidan DJ. Na Bikin Nata. Inda Amaryar Tayi Bayani Irin Jalin Data Tsintsi Kanta Bayan Afkuwar Lamarin.