Jarumi Barkwanci a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Mustapha Naburaska ya bayyana niyyar sa na ƙara aure kwanan nan, bayan mata biyu da ya ke da su a yanzu haka.
Sai dai wani abun mamaki da ya bayyana wanda ya ɗauki hankula, shi ne na matar da ya ayyana a matsayin wacce zai yi wuf da ita a ta 3, tsohuwar jaruma, wacce ta dawo harkar Fim kuma a yanzu, wato Hadiza Kabara.
Mustapha Naburaska, ya ambaci sunan Hadiza Kabara a matsayin wacce ya ke kwankwasawa, wadda kuma nan ba da daɗewa za a yi ji ɓullar labarin lokacin da za a yi bikin na su.
[email protected]