INNA lillahi wa inna ilaihir raji’un! Allah ya yi wa mahaifiyar tsohon Babban Sakataren Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jihar Kano, Alhaji Isma’ila Na-Abba (Afakallahu), rasuwa.
Hajiya Fatima Mu’azu (Gwaggo) ta rasu ne a yau a garin Kano, ta na da shekaru 97.
Za a yi jana’iza anjima da misalin ƙarfe 4:00 na yamma, bayan sallar la’asar a gidan sa da ke unguwar Maidile kusa da masallacin Juma’a na Ansar.
Allah ya jiƙan Gwaggo da rahama, ya kuma albarkaci dukkan abin da ta bari.