Labarai
Gwamnatin Sakkwato Na Yunƙurin Rage Wa Sarkin Musulmi Karfin Iko
Gwamnatin Sakkwato Na Yunƙurin Rage Wa Sarkin Musulmi Karfin Iko
Gwamna Ahmed na Sokoto ya samu amincewar majalisar zartaswar jihar domin mika wani kudiri ga majalisar dokokin jihar da ke neman yin gyara ga dokar da ake da ita na nadi da tsige sarakunan gargajiya a jihar Sokoto. Za a gabatar da kudrin don yin tambari a ranar Litinin
Mafi yawa, kudirin na neman a kwacewa sarkin musulmi gaba daya ikon nadawa, dakatarwa, hukuntashi, mika mulki da dai sauransu, duk wani basaraken gargajiya har zuwa mai unguwa.
Iko daya zai kasance waje daya, kuma ya kasance ga gwamna gaba daya ba tare da tuntubar kowa ba.