E News
Farashin Buhun Siminti Ya Fara Fado Ƙasa Warwas
Da ƊUMI-ƊUMI: Farashin Buhun Siminti Ya Fara Fado Ƙasa Warwas A Najeriya
Rahotanni sun tabbatar da cewa yau a Jihar Kaduna ana sayar da buhun siminti akan Naira 7,000
Hakan ya biyo bayan barazanar da shugaban ƙasar Najeriya Alhaji Bola Ahmed Tinubu ya yi wa manyan kamfanonin siminti.
In baku manta ba watan da ya gabata ne shugaban ƙasa ya umarci kamfanonin da su gaggauta dawo da siminti kan ainihin farashin sa na da, in kuma suka gaza cika wannan umarni na shugaban ƙasa to za a buɗe boda a shigo da siminti ɗan ƙasar waje cewar fadar shugaban ƙasa.
A kwanakin baya dai an siyar da buhun siminti har dubu 10,000 a wasu yankunan kuma 13,000