E News

Farashin Buhun Siminti Ya Fara Fado Ƙasa Warwas

Da ƊUMI-ƊUMI: Farashin Buhun Siminti Ya Fara Fado Ƙasa Warwas A Najeriya

Rahotanni sun tabbatar da cewa yau a Jihar Kaduna ana sayar da buhun siminti akan Naira 7,000

Hakan ya biyo bayan barazanar da shugaban ƙasar Najeriya Alhaji Bola Ahmed Tinubu ya yi wa manyan kamfanonin siminti.

In baku manta ba watan da ya gabata ne shugaban ƙasa ya umarci kamfanonin da su gaggauta dawo da siminti kan ainihin farashin sa na da, in kuma suka gaza cika wannan umarni na shugaban ƙasa to za a buɗe boda a shigo da siminti ɗan ƙasar waje cewar fadar shugaban ƙasa.

A kwanakin baya dai an siyar da buhun siminti har dubu 10,000 a wasu yankunan kuma 13,000

 

Back to top button
error: Content is protected !!