Kannywood

Hadiza Gabon ta Nemi Yafiyar Allah Kan Wani Martani Mai Zafi Da Ta Yi

Shahararriyar jarumar nan ta masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Hadiza Aliyu wacce aka fi sani da Gabon, ta roki gafarar Allah kan wani subutar baki da ta ce ta yi da na sanin yin ta a shafin Twitter a ranar Lahadi.

Tun da farko dai Gabon ta mayar da martani ne ga wani mai amfani da shafin na Twitter ne, bayan ya yi mata kazafi a wani hoto da ta dauka tare da kawayenta kuma abokan sana’arta Rahama Sadau da Fati Washa wanda Rahaman ta wallafa a shafinta.

Hoton dai ya janyo kace-nace a shafukan sada zumunta musamman na Twitter da Instagram inda dukkan jaruman suka sanya a shafukansu.

Wani matashi ne ya fara cin zarafin jaruman inda ya zarge su da yin zina kafin su dauki hoton. Ba da jimawa ba ne ita kuma Hadizan ta mayar masa da martani da cewa da mahifinsa ma suka yi zinar.

Tuni dai Hadiza ta goge wannan sako ta kuma wallafa wani na neman gararar Allah SWT da yin da na sanin mayar da wancan martanin tun da fari.

Shahararriyar jarumar nan ta masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Hadiza Aliyu wacce aka fi sani da Gabon, ta roki gafarar Allah kan wani subutar baki da ta ce ta yi da na sanin yin ta a shafin Twitter a ranar Lahadi.

Tun da farko dai Gabon ta mayar da martani ne ga wani mai amfani da shafin na Twitter ne, bayan ya yi mata kazafi a wani hoto da ta dauka tare da kawayenta kuma abokan sana’arta Rahama Sadau da Fati Washa wanda Rahaman ta wallafa a shafinta.

Hoton dai ya janyo kace-nace a shafukan sada zumunta musamman na Twitter da Instagram inda dukkan jaruman suka sanya a shafukansu.

Wani matashi ne ya fara cin zarafin jaruman inda ya zarge su da yin zina kafin su dauki hoton. Ba da jimawa ba ne ita kuma Hadizan ta mayar masa da martani da cewa da mahifinsa ma suka yi zinar.

Tuni dai Hadiza ta goge wannan sako ta kuma wallafa wani na neman gararar Allah SWT da yin da na sanin mayar da wancan martanin tun da fari.

Fassarar sakon nata ya ce: “Astaghfirul Laah kan martanin da na mayar marar kyau kan wata amsar rashin da’a da wani ya ba ni. Na goge sakon kuma na nemi garafar Allah kan kokarin mayar da martani cikin fushi kan wani kuskuren da aka yi.”

Back to top button
error: Content is protected !!